Dakarun rundunar hadin gwiwa a jihar Borno sun kashe mutane 12 da ake zargin ‘yan ta’addar Boko Haram/ISWAP ne a karamar hukumar Mafa.

Wannan farmakin da aka tare da taimakon bayanan sirri, ya kai ga kawar da maboyar ‘yan ta’adda a Tamsu Ngamdu, Dalakaleri, da Gaza.

Sojojin sun kuma kwato bindigogi kirar AK-47 guda takwas, da harsasai, da magunguna, da kuma kayayyakin jinya.

Hukumomin soji sun yabawa sojojin bisa sabon kwarin gwiwar da suka yi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *